Labaran Yau

Yar Takarar Gwamna Na Jam’iyyar APC Ta Janye Karar Da Takai Kan Zaben Da Ta Gabata A..

Binani ta janye karar Hukumar zabe

Yar takarar Gwamna na jam’iyyar APC Aisha Dahiru Ahmed, wanda aka fi sani da Binani ta janye karar da takai kan zaben da ta gabata.

Takai karar Hukumar zaben ne bayan ta fadi.

Takai karar ne dan kotu tayi duba da hukuncin da Hukumar zabe tayi na canza sakamakon zaben bayan an bayyana ta akan wanda taci daga bakin kwamishinan zabe na Jiha Hudu Yunusa Ari.

Lauyan Binani, Mohammed Sheriff, ya bayyana wa Mai shari’a Inyang Ekwo na kotun tayya Abuja, kan cewa an janye karar Kuma Suna neman kotu ta kawo karshen karar.

Mai shari’a Ekwo ya tunawa sheriff akan cewa an ba shi daman ya bayyana koh karar Tana cikin hurumin kotu koh bata cikin hurumin ta.

Lauyan, ya bayyana wa kotu cewa abubuwa da yawa sun faru tsakanin lokacin da aka daga zaman karar zuwa yanzu, ya roke kotu ta dakile karar.

Mai shari’an yace tunda lauyan yaki bin umurnin kotu dan yin bayanin da suka nema wajen sa. Ya kawo karshen karar a kotun tarayya.

Binani: Wasu daga cikin dalilan da yasa mace barata iya mulki ba ta idon addini

Ni dai Adamawa ina bayan Namiji bana bayan Mace. Domin haramunne mace ta zama itace saman kowa.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button