A kasa da jihohi 19 ne ake ganin za a yi ruwan sama kamar da bakin kwarya wanda ka iya haifar da ambaliya a jihohin da abin ya shafa.
A kasa da jihohi 19 ne ake ganin za a yi ruwan sama kamar da bakin kwarya wanda zai iya haifar da ambaliya a cikin yankunan jihohin da abin ya shafa tsakanin 14 zuwa 18 ga Agusta, 2023.
Jami’in Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Kasa (NEMA), Ko’odinetan Kudu-maso-Yamma, Ibrahim Farinloye, ya ce an yi hasashen hakan ne daga cibiyar gargadin ambaliya (FEWS) Central Hub, Ma’aikatar Muhalli ta Tarayya.
A cewar sakon, ambaliyar za ta shafi wurare kamar haka da muhallinsu:
Aboh a jihar Delta, Ado-Ekiti, a jihar Ekoti, Akure, Idanre, Ifon, Iju Itaogbolu, Ogbese, Owo, Owena, Ondo, a jihar Ondo, Apapa, Badagry, Eti Osa, Ikeja, Ikorodu, Ikoyi, Legas Island, Ojo Lagos, Surulere a Jihar Legas da Ifo, Ota, Sagamu a Jihar Ogun.
Others are, Lafia, Wamba in Nasarawa state, Ikom, Ogoja in Criss River State, Jamaare , Misau, Azare, Itas , Kafin Madaki, Kari, Kirfi, Tafawa Balewa, Katagum in Bauchi State, Hadejia, Miga in Jigawa, Ilesa, Oshogbo a jihar Osun da Kosubosu a jihar Kwara.