Labaran Yau

Tsakaninmu Da Wanda Suka Cutar Damu – Maryam Abacha

Tsakaninmu Da Wanda Suka Cutar Damu – Maryam Abacha

Uwargidan tsohon shugaban kasa, Dakta Maryam Sani Abacha, ta ce lokaci ya yi da za ta yafe wa duk wanda ya zalumce ta da danginta, ta kara da cewa babu wani abu da wani zai yi mata na zalumci da ba za ta iya kawar da kai akan shi ba.

Da take jawabi yayin bikin cikarta shekaru 75 da haihuwa a Abuja ranar Alhamis, Maryam Abacha ta bukaci jama’a da su rungumi yafewa juna domin hadin kai da ci gaban mu.

DOWNLOAD ZIP/MP3

Ta ce; “Daya daga cikin abubuwa masu kyau a rayuwa shine mutane su rungumi ruhin gafara a tsakaninsu. Ya kamata mutane su koyi yadda ake gafarta wa juna. Gafara tana da matukar mahimmanci kamar yadda aka jaddada ta a cikin harsuna da addinai daban-daban. Gafara tana inganta zaman lafiya da sauran alfanu masu yawa na zamantakewa.

“Ina so in yi amfani da wannan dama wajen sanar da duk wanda ke nan da wanda ba ya nan cewa, muna godiya ga Allah Madaukakin Sarki a kan duk abin da ya same mu na alheri ko akasin haka” Inji ta.

Ta yi amfani da wannan dama wajen yi wa kasa addu’ar zaman lafiya, hadin kai, bunkasar tattalin arziki da kuma ci gaban kasa sannan ta nuna damuwarta kan kalubalen tsaro da ke addabar kasar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button