Labaran Yau

Hafsan Sojin Najeriya Gen. Musa Ya Dau Alwashin Daukar Fansar Sojojin Da Aka Kashe A Jihar Niger

Babban hafsan hafsoshin tsaron kasar, Janar Christopher Musa, ya umarci dukkan kwamandojin soji da sojojin kasar da su dauki fansar mutuwar abokan aikinsu.

Ya yi wannan jawabi ne a yayin jana’izar ma’aikatan da ‘yan bindiga suka kashe a jihar Neja ranar Juma’a.

Shugaban tsaron ya sha alwashin cewa wadanda suka yi sanadin mutuwar jami’an za su biya.
Musa ya ce, “Idan ka binne naka, ka ji zafi sosai. Ina so in tabbatar wa iyalai cewa mutuwar su ba a banza ba ne.

“Muna godiya da su. Za mu tabbatar da wadanda suka yi haka dole ne su biya wannan. Ina amfani da wannan dama wajen kira ga dukkan kwamandoji da sojoji a duk fadin Najeriya cewa dole ne mu dauki fansa. Wadanda suka yi haka da wadanda ke ci gaba da kashe mutanenmu a duk inda suke za mu fitar da su daga waje”.

Ya sha alwashin cewa sojoji za su farauto ‘yan fashi, da ‘yan ta’adda da sauran masu aikata laifuka a kasar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button