Labaran YauNEWS

Duk Wanda Zaiyi Takara Ya Ajiye Mukamin Siyasarsa – Majalisar Dattijai

Duk Wanda Zaiyi Takara Ya Ajiye Mukamin Siyasarsa – Majalisar Dattijai

Majalisar Dattijai Ta Bada Umurnin A Jiye Aiki Da Mukamman Siya Ga Duk Mai Neman Tsayawa Takara A Zaben Shekarar 2023

Majalisar Dattijai ta Najeriya ta bakin shugaban ma’aikatan ta, ta bada umarnin ajiye muƙami ga duk masu madafan iko nadaddu don samun damar shiga zaɓen 2023.

DOWNLOAD ZIP/MP3

Cikin wata sanarwa da majalisar ta fitar ta ce wannan yana zuwa ne don bin umarnin sabuwar dokar zaɓe da shugaban ƙasa ya sanyawa hannu ta 2022.

Sanarwar ta ce duk mai rike da mukamin ya ajiye muƙamin nasa daga nan zuwa 11 ga watan Afrilun da muke ciki, ta hanyar mika takarda zuwa ga ofishin mukaddashin shugaban majalisar dattijai na kasa.

Masu karatu me za ku ce?

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button