Labaran YauLabaran Bauchi

DA DUMI DUMI!! Gov Bala Ya Bukaci A Tantace Da Tabbatar Da Sunayen Sabbin Kwamishinoni

Mai Girma Gwamnan Jihar Bauchi Sanata Bala Muhammed Ya Bukaci a Tantance Tare Da Tabbatar Da Sunayen Wadannan Sabbin Kwamishinonin Cike Gurbi Wanda Ya Aikawa Majalisar Dokoki Ta Jihar Bauchi Karkashin Jagorancin Hon Abubakar Y Sulaiman.

SABBIN KWAMISHINONIN CIKE GURBIN SUNE KAMAR HAKA..👇👇👇👇

1) Abdulkadir Ibrahim – Daga Karamar Hukumar Alkaleri

DOWNLOAD ZIP/MP3

2) Zainab Baban Takko – Daga Karamar Hukumar Bauchi Cikin Gari.

3) Adamu Babayo Gabarin – Daga Karamar Hukumar Darazo

4) Maryam Garba Bagel – Daga Karamar Hukumar Dass

5) Dr. Sabiu Abdu Gwalabe – Daga Karamar Hukumar Katagum

6) Ahmed Aliyu Jalam – Daga Karamar Hukumar Dambam

7). Joshua T Sanga DG Ofishin Kula Da Harkokin Kayayyakin Gwamnati

8) Sagir Abdullahi Muhammad. Auditor General

Majalisar Jihar Bauchi Ta Mika ayikin Tantance DG Na Ofishin Kula Da Harkokin Gwamnati Da Kuma Babban Mai Binciken Kudi Ga kwamitocin Kasafin Kudi Da Asusun Gwamnati Tare Da Baiwa kwamitocin Makwanni Biyu Su Gabatar Da Rahotonsu.

Yayin Da Ake Shirin Tantancewa Da Tabbatar Da Sunayen kwamishinonin Cike Gurbin Daga Nan zuwa ranar 7 Ga Satumba, 2022

Allah Ya Basu Ikon Sauke Nauyin Da Allah Ya Dora Musu Ameen Ya Allah 🙏🙏🙏

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button