Labaran YauNEWS

Batun Janye Takaran Shugabancin Nigeria- Bukola Saraki

Batun Janye Takaran Shugabancin Nigeria- Bukola Saraki

Tsohon shugaban majalisar dattawan Nijeriya Ta takwas, Dakta Bukola Saraki, ya shure wasu rahotonnin kafafen sadarwa da suka ce ya janye takarar shugaban kasa ga wani, ya ce shi sam bai janye aniyarsa na neman jagorantar Nijeriya a 2023 ga wani ba.

Saraki wanda tsohon gwamnan jihar Kwara ne, ya ce irin wadannan rahotonnin da ake yadawa da zimmar rage masa karsashin fitowa takara ba zai sanyaya masa guiwa ba, don haka ne ya nemi masu hakan ma da su canza tunani domin burinsa shi ne tabbatar da saita akalar kasar nan daga halin da take ciki a yau.

DOWNLOAD ZIP/MP3

Saraki wanda ke magana ta bakin shugaban kwamitin yakin neman zabensa, Farfesa Lorwuese Hagher, ya nuna kwarin guiwarsa na cewa zai iya samun nasara a wannan kujerar ta shugaban Nijeriya.

A sanarwar da ya raba wa ‘yan jarida a Abuja, Saraki ya jawo hankalin gidajen yada labarai da suke bincike gami da tabbatar da sahihancin batu kafin yadawa domin kauce wa biye wa ‘yan siyasa masu neman cimma burinsu ta kowace fuska.

Saraki ya ce a matsayinsa na mai niyyar fitowa takarar shugaban kasa a yanzu ya maida hankali wajen neman goyon bayan ‘yan Nijeriya a sassa daban-daban domin fito da tsararren tsarin yadda zai fuskanci kalubalen kasar nan.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button