Labaran Yau

Tinubu Ya Sauka Kasar Bissau, Ya Kuma Gana Da Sojojin Najeriya Na Rundunar..

Tinubu Ya Sauka Kasar Bissau, Ya Kuma Gana Da Sojojin Najeriya Na Rundunar ECOWAS

Shugaban Kasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ba da jimawa ba ya sauka kasar Guinea-Bissau gabanin taron kungiyar ECOWAS karo na 63, duka shiri na faruwar taron ya kammala, taron da zaayi a ranar Lahadi 9 ga watan Yuli, amma yayin da Tinubu ya isa Aeroporto International Guinea-Bissau, ya gana da sojojin Najeriya da ke Bissau Bayan Da yake magana da sojojin da ke Bissau.

Tinubu ya yi zaman hoto da su kamar yadda wani mai taimaka wa shugaban kasa ya tabbatar a daren Asabar, 8 ga watan Yuli A ranar Asabar, 8 ga watan Yuli, shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya ziyarci sojojin Najeriya da ke aiwatar da nasu aikin a kasar Bissau a wani bangare na rundunar tabbatar da zaman lafiya ta ECOWAS.

Mai taimakawa shugaban kasa kan harkokin yada labarai Dada Olusegun ne ya bada wannan labari akan shafin sa na Twitter.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button