Labaran Yau

Shugaba Tinubu Tare Da Manyan Mukarraban Sa Sun Halarci Sallar Jummaa A Jihar..

Shugaba Tinubu Tare Da Manyan Mukarraban Sa Sun Halarci Sallar Jummaa A Jihar Lagos

A yau ne Shugaban kasar Nigeria Alhaji Bola Ahmed Tinubu ya halarci sallar Jumuat a babban Masallaci na Ijumota dake Jihar Lagos.

Tare da shi akwai mataimakin gwamnan jihar lagos Hamzat, Babban mai bawa shugaban shawara akan harkar tsaro Mal. Nuhu Ribadu, Shugaban Maaikatan shugaban Kasar kuma tsohon Kakakin Majalisar Wakilai na kasa Femi Gbajabiamilia, Gwamnan Jihar Kogi Yahaya Bello da kuma sauran manyan mukarraben sa.

Shugaba Tinubu zai Ziyarci wasu wuraren yau a jihar ta Lagos domin aiwatar da wasu tsaruka na gwamnatin nasa.

Ga Hotuna Daga Bisani ⇓

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button