Labaran Yau

North East Development Commission Ta Bude Shafinta Don Daukan Matasa Akoya Musu Sana’A

Hukumar Raya Shiyar Arewa Maso Gabas, North East Development Commission, ta bude shafin yanar gizonta, domin daukan matasa maza da mata, wadanda za’a koya musu sana’a. Bayan an koyar da sana’ar Kuma, za’a tallafa musu da kayan sana’ar.

Hukumar ta saba yin wannan lokaci zuwa lokaci. Wannan karon za su koyar da sana’o’in gyaran handset ne da kafa na’urar sattelite, amma wa matasan da ke zaune a Shiyar Arewa Maso Gabas, wato, Jihohin Bauchi, Gombe, Yobe, Borno, Adamawa da Taraba.

Matasa mazauna wadannan jihohin, sai a hanzarta a nema.

DOWNLOAD ZIP/MP3

Ga link din da zakayi Register:

https://admin.nedcresourcecentre.org/register

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button