Labaran YauNEWS

ACF Tayi Allah Wadai Da Yunkurin El-rufai

ACF Tayi Allah Wadai Da Yunkurin El-rufai

Kungiyar Tuntuba ta Arewa ACF ta yi fatali da barazanar da gwamnan jihar Kaduna Malaman Nasir Ahmed El-Rufai ya yi na cewa, za su shigo da sojojin haya daga kasar waje tun da Gwamnatin Tarayya ta gaza tabbatar da tsaro a Nijeriya.

Kurarin na El-Rufai dai ya biyo bayan kara samun aukuwar hare-haren ‘yan bindiga a jihar da kuma harin da su ka kai na bam a kan fasinjojin da ke a cikin jirgin kasan da ya taso daga Abuja zuwa jihar Kaduna a ranar Litinin data wuce, inda iftila’in ya janyo mutuwar fasinjoji tara da kuma sace wasu da dama.

DOWNLOAD ZIP/MP3

ACF a cikin sanarwar da Sakatare Janar dinta Murtala Aliyu ya fitar a jiya Lahadi ta yi nuni da cewa, nauyin Gwamnatin Tarayya ne ta samar da tsaro a Nijeriya, inda kungiyar ta yi kira da samar da mafita kan kalubalen na rashin tsaron.

Kungiyar na rajin kare muradun arewan ta ce. barazanar ta cewa a shigo da sojojin haya don su taya mu yakar ‘yan bindiga, ya zama waji a san kalaman da su ka dace a dinga furtawa kan sha’anin rashin tsaro a Nijeriya. Kungiyar ta yi kira ga gwamoni da Gwamnatin da kuma ‘yan Nijeriya da su guji yin gaggawa kan matsalolin dake addabar kasar nan.

Akan batun yin amfani da jiregen sama na rundunar sojin sama da za yi amfani da su don a yi wa jiragen kasa rakiya daga Abuja zuwa Kaduna da kuma daga Ibadan zuwa Lagos ko zuwa Itakpe don a kauce wa hare-haren ‘yan bindiga, kungiyar ta bayar da shawarar cewa, maimakon yin hakan, kamata ya yi jami’an tsaro su sake tsara yadda suke gudanar da aikin su, tare da kuma aukawa mafakar ‘yan bindigar don su tarwatsa su.

Kungiyar ta yi nuni da cewa, idan jami’an tsaron su ka mayar da hankalin su wajen bai wa hanyoyin na jirgen kasa kadai kariya, ‘yan bindigar za su karkata ne kachokam, wajen kai wa matafiya ta hanya hare-hare.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button