Labaran Yau

Gwamnan Kano Ya Bada Kwamishina Wa Dan Uwan Garo

Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya zabi kwamishinan goma sha tara da mambobin executive council na jiha. Wanda ake jiran amincewar Majalisan jiha.

Cikin wanda aka zaba sun hada da Hon Ali Haruna Makoda tsohon shugaban Ma’aikatan tsohon gwamna Abdullahi Ganduje, da Hon. Nasiru Sule Garo dan uwan dan takarar mataimakin gwamna a jam’iyyar APC a zaben da ta gabata 2023 Murtala Garo. 

Gwamnan ya mika sunayen guda goma sha tara wa Majalisan jiha dan tantancewa.

Shugaban Majalisan jiha Hon. Jibril Ismail Falgore ya bayyana sunayen a zaman ta majalisa ranar talata.

Bayan karanta sunayen, Majalisan ta bukaci wanda aka turo sunayen su da su halarci tantancewa a Majalisan jiha ranar laraba.

Takardar ta bayyana cewa. “Dai dai da karfin da doka gwamnatin Najeriya ta bani, Zan mika takardan sunayen kwamishinan da aka zaba dan tantancewa da amincewa na jihar Kano.

Sunayen da gwamna Abba Kabir Yusuf ya turo sun hada da:

1- Comrade Aminu Abdulsalam

2- Hon. Umar Doguwa

3- Hon. Ali Haruna Makoda 

4- Hon. Labaran Abubakar Yusuf

5- Hon. Danjuma Mahmoud

6- Hon. Musa Shanono

7- Abbas Sani Abbas

8- Haj. Aisha Saji

9- Haj. Ladidi Garko

10- Dr. Marwan Ahmad

11- Engr. Muhd Diggol

12- Hon. Adamu Aliyu Kibiya

13- Dr. Yusuf Kofar Mata

14- Hon Hamza Safiyanu

15- Hon. Tajo Usman Zaura

16- Sheikh Tijjani Auwal

17- Hon. Nasiru Sule Garo 

18- Hon. Haruna Isa Dederi

19- Hon. Baba Halilu Dantiye

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button