Labaran Yau

Gwamna Yusuf Ya Yabawa Ma’aikata Wajen Fitar Shara Mota 600

Gwamna Yusuf Ya Yabawa Ma’aikata Wajen Fitar shara Mota 600

Gwamna Yusuf Abba na Jihar Kano ya yabawa ma’aikatan shara wajen aikin fidda sharan da sukayi a jihar.

Bayanin ta fito daga Jami’in zantarwa na ministirin Muhalli Ismail Gwammaja ranan Litinin a Kano.

Mista Yusuf ya yabawa kwamitin wajen fitar da shara mota 600 a fara aikin su na kwana bakwai.

Ya yi yabon ne yayin da yake karbar rahoto daga hannun mambibin kwamitin da jagorancin ciyaman dinsu Amb Haruna Danzago a karshen sati.

Wanda ya wakilci gwamna Dakta Abdullahi Bichi, Sakataren gwamnatin Jiha yace gwamna ya yabawa wasu kampanin da suka taimaka wajen aikin.

Bayan gode musu dan yin aikinsu, yace suyi kokari dan share duk lungu da sako na garin Kano.

Wannan mulki tazo da kudirin samar lafiya da tsafa na mutane, Yace hakan zai iya yiwu wa ne in an tsafcace gari.

Mista Yusuf ya nemi hadin kan jama’a da su zama masu bin doka wajen taimaka wa wajen ajiye muhallin su a tsaftace.

Ya yace ya bar zuba shara a hanyan ruwa da Kuma zubar wa a ko Ina. Saboda tsafta haqqin kowa ne.

Gwamnatin tace barata daga ido a hakan ba. A karshe Danzago ya bayyana cewa Ma’aikatan a shirye suke dan yin aikin da yakamata dan jindadin jihar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button