Labaran YauNEWS

Suwaye Suka Kai Hari Jirgin Qasa Abuja Kaduna – Bukarti

Suwaye Suka Kai Hari Jirgin Qasa Abuja Kaduna – Bukarti

Masana da masu nazari kan harkokin tsaro a Yammacin Afirka sun bayyana cewa da alama ‘yan kungiyar Ansaru, wacce ke ikirarin kishin Musulunci, ne suka kai hari kan jirgin qasan da ya tashi daga Abuja zuwa Kaduna a watan jiya.

A ranar Laraba ne, wani bidiyo da aka fitar ya nuna wasu daga cikin maharan dauke da bindigogi suna iƙirarin cewa su ne suka sace fasinjojin jirgin ƙasan a ranar Litinin din makon jiya.

DOWNLOAD ZIP/MP3

Bidiyon, wanda bai kai tsawon minti 1:30 ba, ya nuna hudu cikin ‘yan bindigar sanye da kakin sojoji fuskokinsu a rufe a tsaye suna ikirarin ci gaba da riƙe fasinjojin jirgin qasa da suka sace a karshen watan jiya.

Ba a ga fasinjojin a cikin taqaitaccen bidiyon ba, amma mutanen da suka yi maganar sun tabbatar da cewa suna riqe da su.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button