Labaran Yau

Hukumar Kwastam Ta Tabbatar Da Rufe Iyakokin Najeriya Da Nijer

Hukumar Kwastam ta Najeriya ta sanar da rufe dukkan iyakokin kasar da Jamhuriyar Nijar a hukumance

Adewale Adeniyi, mukaddashin kwanturola-janar na NCS, ya yi jawabi ga al’ummar Illela da ke kan iyaka a jihar Sakkwato inda ya jaddada cewa wannan rufe iyakokin ba aikin yaki ba ne. Ya kara da cewa, ana gudanar da shi ne bisa ga umarnin kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ECOWAS, wadda ta dakatar da zirga-zirgar kayayyaki na wani dan lokaci har sai an samu sanarwa.

Adewale ya ci gaba da cewa, aikinsa shi ne nanata umarnin shugaban kasa Bola Tinubu, wanda ke rike da mukamin kwamanda a tarayyar Najeriya da kuma shugaban kungiyar ECOWAS.

Kamar yadda muka sani, daya daga cikin muhimman ayyukan da shugaban ya rataya a wuyansa shi ne saukaka kasuwanci tsakanin kasashen kungiyar ECOWAS. Duk da haka, mun kuma fahimci cewa ciniki ba zai iya bunƙasa ba a yanayin da babu zaman lafiya.
Manufar gwamnati ita ce ta yi amfani da alakar kasuwanci da tsaro yadda ya kamata. Wannan dalili ya sa shugabannin ECOWAS suka yanke shawarar dakatar da kasuwanci da makwabciyar mu ta Jamhuriyar Nijar.
Duk da haka, yana da mahimmanci a ambaci cewa ana aiwatar da wasu matakai, musamman ta hanyoyin diflomasiyya. Ana ci gaba da tattaunawa da mahukuntan Nijar domin warware rikicin cikin lumana.
Don haka ana nufin rufe iyakokin ya zama wani mataki na wucin gadi har sai an cimma matsaya ta karshe na rikicin Jamhuriyar Nijar. Yana da kyau a fayyace cewa babu sanarwar yaki da Jamhuriyar Nijar, kuma ba a yi irin wannan sanarwar ba.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button