Labaran YauNEWS

Ankai Harin Bomb Wata Mashaya A Jihar Taraba

Ankai Harin Bomb Wata Mashaya A Jihar Taraba

Bam ya kashe mutum biyar a Jihar Taraba

Wani harin bam da aka kai a wata mashaya da ke Jihar Taraba a gabashin Najeriya ya kashe aƙalla mutum biyar.

Wasu 19 sun samu munanan raunuka sakamakon fashewar wani abu a garin Iware.

DOWNLOAD ZIP/MP3

Shaidu sun ce an ɓoye bam ɗin ne a cikin wata jaka.

Lamarin ya faru ne da tsakar ranar Talata yayin da mutane suka taru a majalisar da ake shan barasa.

Rundunar ‘yan sandan jihar sun shaida wa manema Labarai cewa ɗaya daga cikin wadanda ake zargi da kai harin ya mutu, amma ba a sani ba ko ɗan ƙunar-bakin-wake ne.

Tashin bomb din yazo da Matukar abin alajabi dubi da jimawan da akayi a kasar Nijeriya  bomb bai tashi ba.

Saidai haryanzu ba’a gano wanda alhakin kai harin ke kansu ba, kuma bawata Kungiya data dauki nauyin kai harin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button