Labaran Yau

Ministocin Tinubu Zasu Fara Aiki Sati Na 3 Cikin Agusta

Ana sa ran ministocin da shugaba Bola Tinubu ya zaba za su fara aiki a mako na uku na watan Agusta, musamman tsakanin ranakun 14 zuwa 18 ga watan Agusta, kamar yadda wata majiya ta kusa da shugaban kasar ta bayyana, babu wani shiri da shugaban ke yi na sabbin ministocin a mako mai zuwa, amma ana sa ran za a saka su cikin jadawalin shugaban kasa a mako na sama..

Kamar yadda aka ruwaito a baya, shugaba Tinubu ya gabatar da jimillar sunayen ministoci 48 ga majalisar dokokin kasar daki-daki. Shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila ne ya gabatar da kashin karshe na jerin sunayen ga majalisar dattawa, yayin da tuni aka fara tantance sunayen ministocin na farko.

Ministers

 

Shugaban kasar ya ki neman ministocin da su zo bakin aiki a mako mai zuwa, domin za su koma babban birnin tarayya (FCT) kuma suna bukatar isasshen lokaci don shirin ayyukan da ke gabansu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button