Labaran Turanci

Sojojin Nijar Sun Hana Sojojin Najeriya Shiga Bosso

Garuruwan Malam Fatori da ke makwabtaka da Najeriya da kuma Bosso a Nijar, wadanda a baya kan samu alaka ta sada zumunta ta yau da kullun tsakanin sojojin Najeriya da sojojin jamhuriyar Nijar a Bosso, yanzu haka suna fuskantar tashin hankali da rashin jituwa saboda abubuwan da suka faru a baya-bayan nan na rashin dai daito tsakanin sojojin da suka karbi mulkin Nijar da kuma gwamnatin Najeriya.

Biyo bayan takunkumin da kungiyar ECOWAS ta kakabawa kasar da kuma ayyana yiwuwar daukar matakin soji, Najeriya da Nijar sun shiga tsaka mai wuya.

Hakan ya sa sojojin Najeriya ke fuskantar koma baya inda aka hana su shiga garin na Bosso domin samun kayayyakin gudanar da rayuwarsu ta yau da kullum da kuma sauran ababen more rayuwa.


Discover more from Labaran Yau

Subscribe to get the latest posts sent to your email.

Join Our:  WhatsApp Group  |  Telegram

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Discover more from Labaran Yau

Subscribe now to keep reading and get access to the full archive.

Continue reading