EntertainmentLabaran Yau

Nahadu Da Mutanen Banza Da Wasu Na Kirki A Masana’antar Fim- Nadiya Adamu

Nahadu Da Mutanen Banza Da Wasu Na Kirki A Masana’antar Fim- Nadiya Adamu

abuwar jaruma a Masana’antar Finafinai ta Kannywwod, NADIYA ADAMU tana daya daga cikin Jaruman da ake ganin sun samu shigowa cikin harkar da kafar dama. Domin kuwa daga shigowar ta fara samun karbwa kuma har ta yi finafinai da dama. A cikin wasu rubutu da ta wallafa a shafinta na sada zumunta ta Instagram  Jarumar ta fayyace  yadda ta taho tun daga Jamhuriyar Nijar domin sha’awar da take da ita ta shiga harkar fim.

A bayaninta ta yi tsokaci akan mutanen Kirkin data hadu dasu a Kannywood dadanda suka taimakatamata da shawarwari tare da bata dama don fitowa a wasu fina finai.

DOWNLOAD ZIP/MP3

Saidai kuma tace akwai tarin mutanen Banza da yawa a cikin harkar a fim,  Musamman idan ke sabuwar jarumace wasu yan 419 wasu kuma masu kokarin yin lalata da jaruma wanda hakan zama ruwan dare da Masana’antar ta Kannywwod.

A kwanakin baya awani shiri na Arewa 24 wanda ake kira da taskar Kannywood wanda Sherif momo ke jagoranta,  yayi zargi Lalata makamaccin  wannan a Masana’antar ta Kannywwod inda yace anayiwa jarumai mata Kan Ta Waye.

Wasu daga cikin jaruman sun musanta wannan zargi,  yayinda ake ganin zargine mai tushe tunda shikanshi jagoran shirin Jarumi ne a Masana’antar.  Kuma hausawa sunce ba’a kwai sai da zakara.

Ko mutane a wani layi zasu dauki ita kanta wannan Jarumar?

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button