
Gwamnan Gombe yayi bakin cikin rashin wazirin Cham
A jawabin darakta janar Na zantarwa na gwamnan jihar Gombe, Muhammad Inuwa Yahaya yayi bakin cikin rasuwan wazirin Cham, Baba KK Cham, wanda ya rasu ran 8 ga Aprailu a shekaran 2023, bayan dogon jinya da yayi.
A wasikar ta’aziyyar da gwamna Muhammad Yahaya Inuwa ya bayyana cewa shi marigayi Nagartacce mutum ne kuma mai fada a ji, shugabane wanda dabi’un sa abun koyone.
Ya kara da cewa ya tuna yanda waziri ya kasance daban da mutane dayawa wajen aiki matuka a Duk inda yayi aiki daga ministri, da sashe sashe zuwa hukumomi wanda ya kawo cigaba a kowani fanni a jihar gombe.
Gwamnan ya mika ta’aziyar sa cikin bakin ciki ga iyali da mutan garin Nidu-gra Cham da cham gabadaya na wannan rashi da akayi.
Marigayi Wazirin Cham ya kasance tsohon ma’aikacin gwamnati, ya aiki a wurare dayawa, tundaga gwamnatin yankin Arewa ta gabas, tsohuwar jihar bauchi wanda yayi ritaya a matsayin maitaimakin darakta.
Kuma gwamnati ta zabeshi a matsayin mamba kakakin hukumar Alhazai na kiristoci, hukumar asusun gida na jihar gombe da kuma hukumar watsa labarai na gombe da sauransu.
Discover more from Labaran Yau
Subscribe to get the latest posts sent to your email.