Labaran YauNEWS

Ramadana- Buhari Yayi Kira Ta Musamman Ga Masu Hali

Ramadana- Buhari Yayi Kira Ta Musamman Ga Masu Hali

 

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya taya al’ummar musulmi a fadin Nigeria da duniya murna dangane da shigowa cikin watan Ramadana wata mai dumbin falala da albarka sai kuma ya bukaci masu hannu da kumbar susa da su taimaka wa mabukata da suke da karamin karfi a cikin al’umma lura da dumbin lada da sada ke da shi a irin wannan watan na Azumi.

DOWNLOAD ZIP/MP3

A sakonsa na taya murna ga al’ummar musulmin Nijeriya da ma duniya baki daya dauke da sanya hannun hadiminsa Malam Garba Shehu, Buhari ya ce wannan damace mai kyau ga masu kudi da su taimaka wa talakawa domin neman tsira duniya da lafiya.

Har-ila-yau, ya kalubalanci musulmai da su kauce wa ayyukan ashsha a cikin wannan watan da ka iya lalata musu ibadansu, ya jawo hankalin al’umma da a dukufa yin ibada da neman yafiya a wajen Allah madauki domin dacewa da falalar da watan ke zuwa da su.

A gefe guda kuma ya yi kira ga masu Azumi da kada su mance da sanya Nijeriya cikin addu’o’in su na neman Allah ya kawo dauki ga kalubalen da suke akwai.

Bai tsaya haka nan ba, ya kuma gargadi musulmai da su guje wa almubazzaranci da kayan abinci a maimakon hakan gara su taimaki talawa da suke fama da yunwa, “Mu taimaki makwafta da abokan zama, talakawa da marasa karfi da suke kusa da mu”.

Buhari ya sake neman addu’o’in neman zaman lafiya da kwanciyar hankali ga Nijeriya da ma duniya, tare da fatan za a yi Azumi cikin aminci da annashuwa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button