Uncategorized

Ganduje Ya Rantsar Da Sabbabin Mambobin Gudanarwa Na APC

Jam’iyyar APC karkashin Jagorancin shugabanta Dr. Abdullahi Ganduje ta kaddamar da mambobin NWC guda 6.

An gudanar da bikin kaddamarwar ne a sakatariyar jam’iyyar ta kasa da ke Abuja a ranar Juma’a da tsakar dare saboda zanga-zangar da ta biyo bayan fitowar sabbin mambobin.

Sabbin mambobin da shugaban jam’iyyar APC na kasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya rantsar, su ne mataimakin shugaban jam’iyyar na kasa (Arewa), Hon. Ali Bukar Dalori; Hon. Garba Datti

DOWNLOAD ZIP/MP3

Muhammad (Mataimakin Shugaban Kasa, Arewa maso Yamma); Farfesa Abdul Karim Abubakar Kana (Mai ba da shawara kan harkokin shari’a na kasa); Hon. Donatus Nwankpa (Sakataren jin dadin kasa); Mary Alile Idele (Shugaban Mata ta Kasa) da Duro Meseko (Mataimakiyar Sakatariyar Yada Labarai ta Kasa).

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button