Labaran Turanci

Hukumar NEMA Ta Bada Sunayen Jihohin Da Za Iya Fuskantar Ambaliya

Hukumar NEMA Ta Bada Sunayen Jihohin Da Za Iya Fuskantar Ambaliya

Hukumar daukin gaggawa na kasa NEMA Ta Bayyana jadawalin sunayen jihohin 14 da garuruwa 13 zasu iya fuskantar ambaliyar ruwa dalilin ruwan da a iya fuskanta Tsakanin 4 ga watan Yuli zuwa 8 ga watan Yuli.

Bayanin tazo daga jawabi da sa hannun Ibrahim Farinloye kodineta na yanki, daga ofishin yanki na Nema na jihar legas.

Farinloye yana magana dan gwamnati da hukumomi masu daukan mataki, suyi kokari su dau matakan da suka kamata dan tsare rai da dukiyar jama’a.

Ya bayyana jihohi da Garuruwan haka:

Jihar Filato: Langtang, Shendam

Jihar Kano: Sumaila, Tudun Wada

Jihar Sokoto: Shagari, Goronyo, Silame

Jihar Delta: Okwe

Jihar Kaduna: Kachia

Jihar Akwa Ibom: Upenekang

Jihar Adamawa: Mubi, Demsa, Song, Mayo Belwa, Jimeta

Jihar Katsina: Katsina, Jibia, Kaita, Bindawa

Jihar Kebbi: Wara, Yelwa, Gwandu

Jihar Zamfara: Shinkafi, Gumi

Jihar Borno: Briyel

Jihar Jigawa: Gwaram

Jihar Kwara: Jebba

Jihar Niger: Mashegu, Kontagora

Farinloye ya godewa Jan kunne da akayi na ambaliya daga Ministirin Muhalli na kasa na Abuja da bada bayanin.

NAN


Discover more from Labaran Yau

Subscribe to get the latest posts sent to your email.

Join Our:  WhatsApp Group  |  Telegram

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

Discover more from Labaran Yau

Subscribe now to keep reading and get access to the full archive.

Continue reading