
Kotu Ta Tabbatar Da Tinubu A Matsayin Zababben Shugaban Kasa
Kotun sauraren kararrakin zaben shugaban kasa ta amince da zaben Bola Tinubu a matsayin shugaban kasa. Kwamitin mutane biyar na alkalai karkashin jagorancin mai shari’a Haruna Tsammani suka bayyana haka a lokacin da suke fadar sakamakon kararrakin da Obi din da Atiku suka shigar a watannin baya kan rashin amincewar su da nasarar ta Tinubu.
Kotun sauraren kararrakin zaben shugaban kasa ta amince da zaben Bola Tinubu a matsayin shugaban kasa.
Alkalan kotun guda biyar karkashin jagorancin Mai shari’a Haruna Tsammani sun bayyana cewa koke-koken Atiku Abubakar na jam’iyyar PDP da Peter Obi na jam’iyyar Labour Party (LP) ba su da inganci, daga bisani suka salami karar.
Discover more from Labaran Yau
Subscribe to get the latest posts sent to your email.