Labaran YauNEWS

Sama Da Layukan Wayoyi Miliyan 73 Sun Shiga Gara- Hukumar NIMC

Sama Da Layukan Wayoyi Miliyan 73 Sun Shiga Gara- Hukumar NIMC

 

Fiye da layukan waya a Nijeriya sama da miliyan 73 na cikin garari sakamakon dakatar da su daga kiran waya saboda kin hada su da lambar dan kasa (NIN).

Datse layukan  ya faru ne sakamakon umarnin da gwamnatin tarayya ta bai wa kamfanonin sadarwa, na cewa duk layin da ba a hada shi da lambar dan kasa ba, to a rufe shi sakamakon wa’adin da aka dauka ya cika.

Wannan umurni yana kunshe a cikin wata sanarwa ta hadin gwiwa wanda jami’in hulda da jama’a na hukumar da ke kula da kamfanonin sadarwa (NCC), Dakta Ikechukwu Adinde da shugaban hukumar kula da katin dan kasa (NIMC), Kayode Olagoke suka fitar. Sun bayyana cewa umurnin ya fara aiki ne tun a ranar Litinin, 4 ga watan Afrilu ya fara aiki.

A cewar sanarwar, ministan sadarwa da tattalin arzikin zamani, Prof Isa Ali Pantami ya ruwaito cewa akwai sama da layukan waya miliyan 125 da aka hada su da lambar dan kasa, yayin da hukumar NIMC take da matsalolin lambar dan kasa sama da miliyan 78.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ne ya bayar da umurnin hada layukan waya da lambar dan kasa tun a watan Disambar 2020, a wani yunkuri da gwamnatinsa take yi wajen samar da tsaro. An dai ta dage karshen wa’adin ranar hada layukan waya da lambar dan kasa, domin a bar ‘yan Nijeriya su sami isasshen lokaci na gudanar da wannan aiki.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button