Labaran TuranciNEWSTrending Updates

Hukumar DSS Tana Tunzura ‘Yan Najeriya Kan Zanga-zanga – Omeyele Sowore

Tinubu ya bukaci ‘yan Najeriya da su ajiye zanga-zangar da suka shirya kuma su ba shi lokaci domin ya mayar da tattalin arzikin kasar

DSS na kara wa wuta gaushi: ‘Yan Najeriya na shirin gabatar da kara a ranar 1 ga watan Agusta domin nuna adawa da wahalhalun da suke fuskanta a karkashin gwamnatin shugaba Bola Tinubu.

Wani mai fafutuka, Omoyele Sowore a ranar Litinin ya ce hukumar tsaro ta farin kaya, DSS, tana gudanar da gagarumin aiki wajen zaburar da ‘yan Najeriya domin gudanar da zanga-zangar ta #EndBadGovernanceInNigeria a ranar 1 ga watan Agusta.

Sowore yana maida martani ne kan matakin da hukumar DSS ta dauka na tsare daya daga cikin masu gangamin zanga-zangar ranar 1 ga watan Agusta da aka fi sani da @Mallam_jabeer.

Wani mai amfani da X(Twitter) mai handle @n6oflife6 ya posting kamar haka:

“Na samu kira daga @Mallam_jabeer cewa hukumar DSS ta tsare shi. Wannan matashin mai zaman lafiya ne kuma ya kasance mai bin doka da oda kan shirye-shiryen zanga-zangar da ya yi.

“Kama shi kafin ranar 1 ga Agusta ba shi da ma’ana. Ana kokarin ganin an sako shi. Najeriya mun gode muku.”

Omeyele Sowore, da yake mayar da martani, ya rubuta:

“Hukumar @OfficialDSSNG tana yin aiki mai ban sha’awa don tayar da #EndBadGovernanceInNigeria tawaye. #FreeJabirNow.”

Join Our:  WhatsApp Group  |  Telegram

Watch African Stories

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button