
Rahotanni sun bayyana cewa kungiyar kwallon kafa ta Paris Saint Germain (PSG) ta ki biyan bashin Kylian Mbappe kusan fam miliyan £50 a matsayin albashi mai tsoka duk da cewa an tilasta mata yin hakan.
Hukumar LFP, mai kula da harkokin kwallon kafa ta Faransa, ta umurci zakarun gasar Faransa ta League 1 da su biya Mbappe kudaden shi na tallafi da albashin da ba a biya ba daga zamansa na tsawon shekaru bakwai a birnin Paris, amma sun bayyana cewa ba za su biya ba.

Ana kyautata zaton Mbappe ya tuntubi UEFA a watan da ya gabata kan rashin jituwar albashi.
A sanarwar kungiyar ta ce kamar haka:
“Idan akayi la’akari da iyakokin doka na kwamitin don yanke hukunci game da wannan shari’ar, yanzu dole ne a garzaya da shari’ar a gaban wani hukumci, wanda PSG za ta yi farin cikin gabatar da duk gaskiyar a cikin watanni da shekaru masu zuwa.“

P.S.G dai ta ji takaicin Mbappé bayan tayi masa tayin mafi tsada a tarihin kungiyar, wadda ya kulla a shekarar 2022. Sai dai Mbappé bai gamsu ba saboda yana ganin an karya alkawarin da ya dauka na sayen manyan ‘yan wasa.
Discover more from Labaran Yau
Subscribe to get the latest posts sent to your email.