Labaran Yau

Buhari Ya Tafi London Nadin Sarautan King…

Buhari Ya Tafi London Nadin Sarautan King Charles lll

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ran laraba zai tafi landan ya hadu da shugabanin kasashen duniya, dan zuwa gayyata na Binkin nadin sarautar King Charles na uku da matansa Camilla na zama sarki da sauraniyar burtaniya.

Mai bada shawara wa Shugaban kasa kan shafin zantarwa Femi Adesina. Ya bayyana hakan ranan laraba.

“Bayan Nadin sarautar, kunyiyar Commonwealth zasu ci moriyar haduwan shugabannin duniya. Wanda zata yi zama da Shugabanin kasashen gaba daya ranan jumma’a 5 ga watan Mayu”
A cewar sa.

Ya kara cewa Shugaban kasan zai amshi gayyata commonwealth dan ya tattauna kan matsalolin matasa da kuma cigaban commonwealth.

King Charles ya hau kujerar sarautar burtaniya ran 8 ga watan satumba 2022 bayan mutuwar Mahaifiyar shi Sarauniya Elizabeth ta biyu.

Tawagan Buhari sun hada da Sakataren Gwamnatin tarayya Mustapha Boss, Ministan Al’amuran waje Geoffrey Onyeama, Ministan Zantarwa da Al’ada Lai Mohammed, Mai bada shawaran tsaro na kasa Babagana Monguno, Darakta Janar na NIA Ahmed Abubakar, shugabar NIDCOM Abike Dabiri-Erewa da wasu manyan jami’u.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button