Labaran Yau

Wata Mata Ta Kashe Mijinta Bisa Cece – Kuce Da Sukayi Kan….

Wata Mata Ta Kashe Mijinta Bisa Cece – Kuce Da Sukayi Kan Taliyar Indomie

Wata mata mai shayarwa mai suna Damilola Opeyemi, ta shiga hannun jami’an tsaro bayan da ta daba wa mijinta wuka a lokacin da suke takaddama a kan cin abinci.

Lamarin ya faru ne a gidan ma’auratan da ke unguwar Adogba Ajegede da ke Ibadan a jihar Oyo.
Rikicin da ya barke tsakanin Damilola Opeyemi da mijinta mai shekaru 27, Oluwashina, ya taso ne a kan shirin cin abincin da suka yi wanda ya hada da taliyar Indomie noodles.

Yayin barkewar rikicin nasu, Damilola Opeyemi ta yi zargin cewa ta yi amfani da wuka ne, inda ta yi wa mijinta rauni mai muni. Duk da an garzaya da shi asibiti, Oluwashina ya kasa shawo kan raunukan da ya samu, kuma ya rasu.

Bayan faruwar lamarin, jami’an tsaro sun kama matar, Damilola, inda aka kai gawar marigayin zuwa dakin ajiyar gawa.

Rundunar ‘yan sandan ta mika Damilola gidan yari dangane da faruwar lamarin har sai an yanke mata hukunci.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button