Labaran Yau

Tinubu Ya Aika Shugaban Hukumar Katin Shaidar Dan Kasa NIMC Hutun Tilas, Ya Nada Shugaban Riko

Shugaba Bola Tinubu ya umurci Darakta-Janar/Shugaba na Hukumar Kula da Shaida ta Kasa (NIMC), Engr. Aliyu Abubakar Aziz zai fara hutun kwanaki 90 kafin ya yi ritaya.

A cikin wata sanarwa da mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai da Ajuri Ngelale ya fitar, ya ce hutun zai fara aiki ne daga ranar 24 ga watan Agustan 2023, wanda zai kai ga yin ritaya daga aiki a ranar 24 ga Nuwamba, 2023.

“Shugaban kasa ya amince da nadin Engr. Bisoye Coker-Odusote zai yi aiki a matsayin mukaddashin Darakta-Janar/Shugaba na Hukumar Kula da Shaida ta Kasa (NIMC) na tsawon kwanaki 90, daga ranar 24 ga Agusta, 2023, bayan haka, zai fara cikakken wa’adin shekaru hudu a matsayin jagoran hukumar NIMC. Darakta-Janar / Shugaba, daga ranar 24 ga Nuwamba, 2023, ”in ji sanarwar.

Shugaban ya kuma amince da nadin Hon. Yusuf Buba Yakub don yin aiki a matsayin Darakta/Shugaba na Directorate of Technical Aid Corps (DTAC).
“Wannan ya biyo bayan cikar wa’adin tsohon Daraktan DTAC, Dokta Pius Osunyikanmi.”
“Shugaba Tinubu ya umurci wadanda aka nada da su fara aiki nan take.”

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button