Labaran Yau

Sudan Na Gab Da Fuskantar Yakin Basasa, Inji Shugaban Majalisar Dinkin…

Sudan Na Gab Da Fuskantar Yakin Basasa, Inji Shugaban Majalisar Dinkin Duniya Guterres

António Guterres ya yi Allah wadai da rashin mutunta dokar kare hakkin dan adam kamar yadda aka yi tashe-tashen hankula a jihohi da dama na Sudan.
Sudan na gab da shiga “cikakken yakin basasa” wanda zai iya lalata zaman lafiyar yankin baki daya, kamar yadda Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin, bayan wani hari ta sama da aka kai a wani yanki ya kashe fararen hula kusan mutum 22.

Rahoton ya zo cewa “mutane 22 sun mutu tare da wasu da suka jikkata duka fararen hula” sakamakon harin da aka kai wani gari cikin birnin Khartoum Omdurman, a gundumar Dar al-Salam.

Watanni uku kenan ana yaki tsakanin hafsan hafsoshin Sudan da ke hamayya da juna, wannan farmakin shi ne na baya bayan nan da ya tayar da hankali.

Akalla mutane 3,000 ne aka kashe yayin da wasu 6,000 suka jikkata a rikicin, wadanda suka tsira sun ba da rahoton cin zarafi na lalata da kuma shaidu sun yi magana game da kisan gilla na kabilanci. Sace sacen dukiyar jama’a, daga bisani Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin yiwuwar aikata laifukan cin zarafin bil’adama a yankin Darfur.

Wani faifan bidiyo da ma’aikatar lafiya ta wallafa a Facebook ya nuna gawarwakin da babu rai bayan tashin bam a ranar Asabar, ciki har da mata da dama. Marubucin ya ce mazauna garin “sun kidaya matattu 22”.

Dakarun Rapid Support Forces (RSF) da ke yaki da sojojin, sun ce bam din ya kashe 31 tare da zargin sojoji da aikata hakan. Rundunar sojin ta musanta wannan zargi, inda ta ce a wata sanarwa da ta fitar a ranar Lahadin da ta gabata, rundunar sojin sama ba ta kai wani hari ba a birnin a ranar da ta gabata.

Tun lokacin da aka fara yakin, jami’an tsaro sun kafa sansanoni a wuraren zama, kuma ana zarginsu da tilastawa fararen hula barin gidajensu.

Sakatare-janar na Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres, a jiya Lahadi ya yi Allah wadai da harin da aka kai a Omdurman, wani birni da ke kan gabar kogin Nilu daga birnin Khartoum, yana mai cewa “an ba da rahoton kashe akalla mutane 22” tare da raunata da dama, in ji mataimakinsa Farhan Haq a cikin wata sanarwa.

Guterres “ya nuna matukar damuwa cewa yakin da ake ci gaba da gwabzawa tsakanin dakarun soji ya jefa kasar Sudan cikin wani mummunan yakin basasa, wanda zai iya dagula zaman lafiyar yankin baki daya”, in ji Haq.

“Akwai rashin mutunta dokokin jin kai da kare hakkin dan adam wanda ke da hadari da damuwa.”

An yi artabu tsakanin sojoji da RSF a wasu wurare a Sudan a ranar Lahadi, ciki har da jihohin Arewacin Kordofan, Kudancin Kordofan da Blue Nile.

Akalla mutane miliyan 3 rikicin Sudan ya raba da muhallansu, daga cikinsu akwai kusan dubu 700 da suka yi gudun hijira zuwa kasashe makwabta, a cewar kungiyar kula da ‘yan gudun hijira ta duniya.

Majalisar Dinkin Duniya da kungiyoyin Afirka sun yi gargadin “kabilanci” game da rikici a yammacin yankin Darfur, inda Amurka, Norway da Birtaniya suka zargi RSF da mayakan Sa-kai da alhakin yawancin cin zarafin da suka auku.

Haq ya bayyana goyon bayansa ga kokarin kungiyar tarayyar Afrika da kungiyar Igad ta gabacin Afrika na kawo karshen rikicin Sudan.

A yau litinin shugabannin kasashen Habasha, Kenya, Somaliya da Sudan ta Kudu – ‘yan kungiyar Igad dake rike da rahotanni sahihai daga Sudan za su gana a Addis Ababa.

An gayyaci hafsan sojojin Sudan, Janar Abdel Fattah al-Burhan, da kwamandan RSF, Janar Mohamed Hamdan Daglo, amma babu wani bangare da ya tabbatar da cewa zai halacci taron.

An sanar da tsagaita wuta da dama a yakin kuma an yi watsi da su.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button