Labaran YauNEWS

Saudiya Zata Samar Da Abincin Buda Baki Na Azumi Wa Kashe 34

Saudiya Zata Samar Da Abincin Buda Baki Na Azumi Wa Kashe 34

 

Kasar Saudiyya za ta kaddamar da wani shirin buda baki a kimanin kasashe 34, kamar yadda kamfanin dillancin labaran kasar ya ruwaito a ranar laraba. 

Hukumar yada labaran ta rawaito cewa, manufar shirin shi ne samar da abincin buda baki ga Musulmi a cikin watan Ramadan, wanda ake fatan soma wa a ranar 2 ga watan Afrilu.

DOWNLOAD ZIP/MP3

Ana sa ran mutum miliyan 1.2 za su ci gajiyar shirin.

Rahotannin sun ce Ma’aikatar kula da harkokin addinin musulunci, ta yi dukkanin shirye-shiryen da suka wajaba domin ganin shirin ya shafi bangarorin duniya, ko da yake Hukumar tace ya dogara daga yanayin kasashe dake neman bukata.

Za a aiwatar da shirin ne tare da hadin gwiwar ofisoshin jakadancin Saudiyya da cibiyoyin addinin Musulunci na ma’aikatar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button