Labaran Yau

Hukumar Immigration Tayin Karin Girma Wa Ma’aikata 7000

Hukumar Immigration Tayin Karin Girma Wa Ma’aikata 7000

Sama da Jami’ai ta Hukumar Immigration ne suka samu karin matsayi a Ofishin su ta jihohi gaba daya a kasar.

Karin girman yazo ne ta wasika da saka hannun sakataren hukumar Sibil difens, immigration, gidan gyara hali da fire service, Alhaji Jafaru Ahmed.

A Jawabin jiya da sa hannun mai rikon kwaryar Mai zantarwa PRO ta Hukumar Mista Kenneth Kure, wanda ya samu karin girma zuwa mataimakin kwantrola, wanda suka samu karin girman sun hada da manyan jami’ai wanda suka zauna wa jarabawan da kuma kananan jami’ai wanda suka samu karin girman saboda karin takardu.

Mai rikon kwaryar kwanturola Janar na Immigration Wuraola Adepoju, Ta kawo kwanturola goma sha biyu na wasu jihohi wanda sun hada da birnin tarayya Abuja, Kano, jigawa, Ondo, Ogun da sauransu.

Ta amince da zaben mai magana da yawun erstwhile service Tony Akuneme a matsayin kwanturola ta Birnin tarayya Abuja, kwanturola Joseph Dada ya zama principal staff officer na ofishin kwanturola janar.

A Jawabin da tayi wa jami’an wajen paretin wata, ta ja musu kunne wajen saka aikin su farko ba san zuciya ba.

Tayi alkawarin kula da lamarin jin kai na Ma’aikatan, Kuma karin girma zai samu ne ta hanyar wanda ya fara shiga.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button