Labaran Yau

Akume Ya Fara Aiki A Matsayin Sakataren Gwamnatin Tarayya

fara Aikin George Akume a matsayin Sakataren Gwamnatin Tarayya

Sabon sakataren Gwamnatin Tarayya George Akume, ya fara aiki ranan Laraba da alkawarin sa ido da tsare tsare da gudanarwa dokokin gwamnati.

Kamin zaben shi a matsayin Sakataren gwamnatin tarayya, Akume ya kasance gwamna na tenure biyu a jihar Benue daga shekarar 1999 zuwa 2007.

Ya samu matsayin ministan Special duties da gudanarwar gwamnati, a mulkin tsohon shugaban kasa Muhammadu buhari.

Nuna jin dadin sa wa tsohon Sakataren gwamnati,
Boss Mustapha,dan gudanar da canjin gwamnati cikin tsafta da Lumana da yayi. Akume Yace aiki a ofishin SGF yana da dan wuya. Zai nashi kokari daga inda tsohon SGF ya tsaya.

“Zamuyi iya kokarin mu dan kare muradun kasar, Ina da budaddiyar doka Kuma Zamu cigaba da iya kokarin mu, daga inda ka tsaya.

Akume ya yabawa shugaban kasa Bola Tinubu da ya bashi daman yin aiki wa kasar sa.

Mustapha yace yaji da ya kasance yana nan wajen miqa karagar mulki da gudanarwar na Ofishin Sakataren gwamnati tarayya wa Akume.

Ya Kuma bayyana wa Akume abubuwan da suke kunshe cikin aikin Sakataren gwamnati.

Mustafa ya bashi bayani akan abubuwa da suke ba a kammala su ba.

Daily Nigeria ta rawaito

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button